Wani dan tasi ne ya dauko yara daga makaranta, sai wani daga cikinsu ya yi ta surutu, yana karatun da aka koya masu a ranar, yana cewa: “Idan babana sarki ne, mamata sarauniya, zan zama yarima.” dan tasi ya damu kwarai,
sai ya ce wa yaron: “Idan babanka dan fashi ne fa, kuma innarka karuwa, kai kuma me za ka zama?” Sai (yaro) ya ce: “Sai in zama dan tasi kamarka!”
wani saurayi ne yana zaune a gaban gidan su sai yaga wata yarinya taxo xata wuce yana ganin ta sai yaji ta kwanta mishi aransa ae kuwa baiyi kasa a gwiwa ba yaje yayi mata sallama ta amsa mishi sai yace baiwar Allah idan baxa ki damu ba ina dan so ki bani 1minute xan danyi magana dake ne sai tace ba damuwa.... Malama agaskia baxan 6oye miki ba tunda na ganki sai naji kinyi min ma'ana naji ina matukar son ki a raina.... Idan baxa ki damu ba xanso naji sunan malaman... Kuma xanso da ki bani full Address naki... Tayi shiru na dan wasu seconds ba tare da tace komai ba... Tana juyo wa sai ta daga hannu ta shimfida masa mari tace haba malam ka kalle ni ka kalle ka kace wai ni kake so plz na wuce da sanin ka kaje ka nemi dai-dai dakai.... Ba tare da yace mata komai ba sai ya juya ya tafi abin yayi masa matukar ciwo a xuciyar sa amman haka ya danne xuciyarsa.... bayan kamar 2weeks haka yana xaune a gaban gida inda ya saba xama sai yaji anyi masa sallama cikin wata sassanyar murya sai ya amsa sallaman sannan kuma ya daga kansa domin ganin wanda yayi masa sallaman yana daga kansa sai yaga Ashe wannan yarinya ce wanda ya ta6a tare wa 2weeks da suka wuce... Sai tace bawan Allah nasan xa kayi mamakin gani na amman kuma ba abin mamaki bane... Tun randa wannan abu ya faru na kasa samun sukuni a cikin xuciyata... Na kuma kasa samun nutsuwa araina... Sai naji cikin ikon Allah bayan faruwar wannan Abu sainaji na kamu da son ka araina... kuma ni yanxu nayi nadama abin da nayi maka plz ina so ka yafe min kuma ina so ka amsa soyayyah ta.... Wai yanxu idan kaine hakan ta faru da kai wani irin Answer za ka bawa wannan yarinyar...???
No comments:
Post a Comment