Tuesday, January 29, 2019

Hira tsakanin saurayi da budurwa

Wani saurayi ne yaje wajen budurwar sa hira suna cikin hirar sai NEPA suka kawo wuta sai ya tambaye ta yace yanaga ko, ina da wuta amma banda gidan ku?


Sai tace wlh lokacin ana ruwan sama shine iska ta tsinke WAYAR. Sai yace to meyasa baku kira YAN NEPA sun
gyara ba?

Sai tace, wallahi mun kira su sunce zasu zo gashi yau har kwana biyu shuru. Sai yace bakomai, abinda za,ayi shiga gida kisa YARA SU FITOMIN DA TSANI DA KUMA FILAYA.


Sai tace haba kawai ka barshi za,a gyara, SWEET HEART kaga ba aikin ka bane. sai yace haba MY LOVELY ai abun duk bigene.

Aka fitomai da TSANI DA SAURAN KAYAN AIKI ya hau FALWAYA ya fara aiki. Can zuwa wani dan lokaci sai budurwar sa taji yayi wani MUGUN IHU HADE DA KARA wuta ta jaho sa kasa ya fado cikin KWATA A SUME.


Bayan ya farfado daga suman da yayi, ya tashi zaune yana daga kansa sai yaga budurwar sa da baban ta da babarta da yaran gidan gaba daya da kuma sauran yaran unguwar suna mai sannu.



Can saiji yayi wata karamar yarinya kanwar budurwar sa tace, LA! AUNTY SAURAYIN KI YAYI KASHI A WANDO.
Hahahaha!

No comments:

Post a Comment